1Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu;
2Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga,
3Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata,
4wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila,
5Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf
6Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku;
7Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku,
8“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku,
9Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku;
10Ni ne Ubangiji Allahnku
11“Amma mutanena ba su saurare ni ba;
12Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare
13“A ce mutanena za su saurare ni,
14da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu
15Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki,
16Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau;