1Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah?
2Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa,
3Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai,
4Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu;
5Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura
6Sun ragargaje dukan sassaƙar katako
7Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus;
8Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!”
9Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba;
10Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah?
11Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama?
12Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa;
13Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka;
14Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa
15Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka;
16Yini naka ne, dare kuma naka ne;
17Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya;
18Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji,
19Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji;
20Ka kula da alkawarinka,
21Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya;
22Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka;
23Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka,