1A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka;
2Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka;
3Ka zama dutsena da kagarata,
4Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye,
5Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka,
6Daga haihuwa na dogara gare ka;
7Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci,
8Bakina ya cika da yabonka,
9Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa;
10Gama abokan gābana suna magana a kaina;
11Suna cewa, “Allah ya yashe shi;
12Kada ka yi nisa da ni, ya Allah;
13Bari masu zagina su hallaka da kunya;
14Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya;
15Bakina zai ba da labarin adalcinka,
16Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka;
17Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini
18Ko sa’ad da na tsufa da furfura,
19Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah,
20Ko da yake ka sa na ga wahaloli,
21Za ka ƙara girmana
22Zan yabe ka da garaya
23Leɓunana za su yi sowa don farin ciki
24Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci