1Ka cece ni, ya Allah,
2Na nutse cikin laka mai zurfi,
3Na gaji da kira ina neman taimako;
4Waɗanda suke ƙina ba dalili
5Ka san wautata, ya Allah;
6Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka
7Gama na jimre da ba’a saboda kai,
8Ni baƙo ne a cikin ’yan’uwana,
9gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata,
10Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi
11sa’ad da na sanya rigunan makoki,
12Masu zama a ƙofa suna mini ba’a,
13Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji,
14Ka fid da ni daga laka,
15Kada ka bar rigyawa yă sha kaina
16Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka;
17Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka;
18Ka zo kusa ka kuɓutar da ni;
19Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya;
20Ba’a ta sa zuciyata ta karai
21Sun sa abin ɗaci cikin abincina
22Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko;
23Bari idanunsu yă dushe don kada su gani,
24Ka kwarara fushinka a kansu;
25Bari wurinsu yă zama kufai;
26Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta
27Ka neme su da laifi a kan laifi;
28Bari a shafe su sarai daga littafin rai
29Ina cikin zafi da kuma azaba;
30Zan yabe sunan Allah cikin waƙa
31Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya,
32Matalauta za su gani su kuma yi murna,
33Ubangiji yakan ji masu bukata
34Bari sama da ƙasa su yabe shi,
35gama Allah zai cece Sihiyona
36’ya’yan bayinsa za su gāje ta,