1Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka
2Gama kibiyoyinka sun soke ni,
3Saboda hasalarka babu lafiya a jikina;
4Laifofina sun mamaye ni
5Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari
6An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni;
7Bayana yana fama da zazzaɓi;
8Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni;
9Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji;
10Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare,
11Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna;
12Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu,
13Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji,
14Na zama kamar mutumin da ba ya ji,
15Na dogara gare ka, ya Ubangiji;
16Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina
17Gama ina gab da fāɗuwa,
18Na furta laifina;
19Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi;
20Waɗanda suke sāka alherina da mugunta,
21Ya Ubangiji, kada ka yashe ni;
22Zo da sauri ka taimake ni,