1Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji,
2Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni,
3gama ƙaunarka kullum tana a gabana,
4Ba na zama tare da masu ruɗu,
5na ƙi jinin taron masu aikata mugunta
6Na wanke hannuwana cikin rashin laifi,
7ina shelar yabonka da ƙarfi
8Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji,
9Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi
10waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu,
11Amma na yi rayuwa marar zargi;
12Ƙafafuna suna tsaye daram;