1Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi;
2Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan,
3su da ya tattara daga ƙasashe,
4Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada,
5Sun ji yunwa da ƙishirwa,
6Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
7Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya
8Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
9gama yana shayar da masu ƙishirwa
10Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,
11gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah
12Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya;
13Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
14Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai
15Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
16gama ya farfashe ƙofofin tagulla
17Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa
18Ba su so su ga abinci ba
19Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
20Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su
21Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
22Bari su miƙa hadaya ta godiya
23Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa;
24Sun ga ayyukan Ubangiji,
25Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi
26Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa;
27Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu;
28Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu,
29Ya kwantar da hadiri suka yi tsit;
30Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta,
31Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa
32Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane
33Ya mai da koguna suka zama hamada,
34ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani,
35Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa
36a can ya kai mayunwata su yi zama,
37Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi
38ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru,
39Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su
40shi da yake kawo reni a kan manyan mutane
41Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu
42Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki
43Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa