1Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa;
2Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi;
3Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki;
4Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa;
5Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi,
6Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa,
7Shi ne Ubangiji Allahnmu;
8Yana tuna da alkawarinsa har abada,
9alkawarin da ya yi da Ibrahim,
10Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida,
11“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana
12Sa’ad da suke kima kawai,
13suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma,
14Bai bar kowa yă danne su ba;
15“Kada ku taɓa shafaffena;
16Ya sauko da yunwa a kan ƙasa
17ya kuma aiki mutum a gabansu,
18Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa
19sai abin da ya rigafaɗi ya cika
20Sarki ya aika aka kuma sake shi,
21Ya mai da shi shugaban gidansa,
22don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama
23Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar;
24Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa;
25waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa
26Ya aiki Musa bawansa,
27Suka yi mu’ujizansa a cikinsu,
28Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu,
29Ya mai da ruwaye suka zama jini,
30Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi,
31Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito,
32Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara,
33ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu
34Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito,
35suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu,
36Sa’an nan ya karkashe dukan ’yan fari a cikin ƙasarsu,
37Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya,
38Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi,
39Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi,
40Suka roƙa, ya kuwa ba su makware
41Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo,
42Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki
43Ya fitar da mutanensa da farin ciki,
44ya ba su ƙasashen al’ummai,
45don su kiyaye farillansa