1Yabi Ubangiji, ya raina.
2Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga
3ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye.
4Ya mai da iska suka zama ’yan saƙonsa
5Ya kafa duniya a kan tussanta;
6Ka rufe ta da zurfi kamar da riga
7Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu
8suka gudu a bisa duwatsu,
9Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa;
10Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka;
11Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji;
12Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan;
13Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama;
14Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu,
15ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna,
16Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai,
17A can tsuntsaye suke sheƙunnansu;
18Manyan duwatsu na awakin jeji ne;
19Wata ne ke ƙididdigar lokuta,
20Ka yi duhu, sai ya zama dare,
21Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta
22Rana ta fito, sai suka koma shiru;
23Mutum yakan tafi aikinsa,
24Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji!
25Akwai teku, babba da kuma fāɗi,
26A can jiragen ruwa suna kai komo,
27Waɗannan duka suna dogara gare ka
28Sa’ad da ba su da shi,
29Sa’ad da ka ɓoye fuskarka,
30Sa’ad da ka aika da Ruhunka,
31Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada;
32shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana,
33Zan rera ga Ubangiji dukan raina;
34Bari tunanina yă gamshe shi,
35Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya