1Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa?
2Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi,
3Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa;
4Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah;
5Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara;
6Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni;
7Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana;
8Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka;
9Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki.
10Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi;
11Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta;
12Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah.
13Don me mugun mutum zai ƙi Allah?
14Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki;
15Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum;
16Ubangiji Sarkin har abada abadin ne;
17Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala;
18kana kāre marayu da waɗanda aka danne,