1Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata
2don ka ci gaba da yin kome daidai
3Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma,
4amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya,
5Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa;
6Ba ta wani tunanin rayuwa;
7Yanzu fa, ’ya’yana, ku saurare ni;
8Ku yi nesa da hanyarta,
9don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu
10don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku
11A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi,
12Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo!
13Ban yi biyayya da malamaina ba
14Na zo gab da hallaka gaba ɗaya
15Ku sha ruwa daga tankinku,
16In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje,
17Bari su zama naka kaɗai,
18Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka,
19Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani,
20Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali?
21Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji,
22Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi;
23Zai mutu saboda rashin ɗa’a