1Ɗana, kada ka manta da koyarwata,
2gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa
3Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai;
4Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau
5Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka
6cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi,
7Kada ka zama mai hikima a ganinka;
8Wannan zai ba wa jikinka lafiya
9Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka,
10ta haka rumbunanka za su cika har su zuba,
11Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji
12domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna,
13Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima,
14gama ta fi azurfa riba
15Ta fi lu’ulu’u daraja;
16Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama;
17Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi,
18Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta;
19Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya,
20ta wurin sani aka rarraba zurfafa,
21Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira,
22za su zama rai a gare ka,
23Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya,
24sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba;
25Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya
26gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka
27Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace,
28Kada ka ce wa maƙwabcinka
29Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka,
30Kada ka zargi mutum ba dalili,
31Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye
32Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta
33La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye,
34Yakan yi wa masu girman kai ba’a
35Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna,