1Ɗana, in ka yarda da kalmomina
2kana kasa kunne ga abin da yake na hikima,
3in kuma ka kira ga tsinkaya
4in ka neme shi yadda ake neman azurfa
5to, za ka gane tsoron Ubangiji
6Gama Ubangiji yana ba da hikima,
7Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya,
8gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata
9Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci
10Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka,
11Tsinkaya za tă tsare ka,
12Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane,
13waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi
14waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau
15waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne
16Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya,
17wadda ta bar mijin ƙuruciyarta
18Gama gidanta yana kai ga mutuwa
19Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa
20Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki
21Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar,
22amma za a fid da mugaye daga ƙasar,