1Kada ka yi ƙyashin mugaye,
2gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3Ta wurin hikima ce ake gina gida,
4ta wurin sani ɗakunanta sukan cika
5Mutum mai hikima yana da iko sosai,
6don yin yaƙi kana bukatar bishewa,
7Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai
8Duk mai ƙulla mugunta
9Makircin wawa zunubi ne,
10In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala,
11Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su;
12In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,”
13Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau;
14Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai;
15Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali,
16gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma,
17Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi;
18in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba
19Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta
20gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba,
21Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana,
22gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan,
23Waɗannan ma maganganun masu hikima ne,
24Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”,
25Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi,
26Amsa da take ta gaskiya
27Ka gama aikinka
28Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba,
29Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini;
30Na wuce cikin gonar rago,
31ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina,
32Na yi tunani a zuciyata
33Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi,
34sai talauci ya shigo maka kamar ’yan fashi