1Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata
3Ka sha ɗamara kamar namiji;
4“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya?
5Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani!
6A kan me aka kafa tushenta,
7yayinda taurarin safe suke waƙa tare
8“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi,
9Lokacin da na yi wa gizagizai riga
10sa’ad da na yi masa iyaka na
11Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai,
12“Ko ka taɓa ba safiya umarni
13don ta kama gefen duniya
14Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi;
15An hana mugaye haskensu,
16“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku,
17Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa?
18Ko ka gane fāɗin duniya?
19“Ina ne hanyar zuwa gidan haske?
20Ko za ka iya kai su wurarensu?
21Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin!
22“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara
23waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala,
24Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya,
25Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa,
26don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin
27don a ƙosar da wurin da ya bushe
28Ruwan sama yana da mahaifi?
29Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara?
30lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse,
31“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da ’ya’yanta?
32Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu
33Ka san dokokin sammai?
34“Za ka iya tsawata wa gizagizai
35Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa?
36Wane ne yake cika zuciya da hikima
37Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai?
38sa’ad da ƙura ta yi yawa
39“Za ka iya farauto wa zakanya nama,
40Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu,
41Wane ne yake ba hankaka abinci