1Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah?
3Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne?
4“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka
5Ba muguntarka ce ta yi yawa ba?
6Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili;
7Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba
8Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa,
9Ka kori gwauraye hannu wofi,
10Shi ya sa kake kewaye da tarkuna,
11An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani,
12“Ba Allah ne a can sama ba?
13Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani?
14Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu
15Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar
16An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika,
17Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu!
18Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau,
19“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi;
20‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu,
21“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa;
22Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa
23In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke.
24Ka jefar da zinariyarka a ƙasa,
25sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka,
26Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki
27Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka,
28Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki,
29Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’
30Zai ceci wanda ma yake mai laifi,