1Abin da Allah ya faɗa game da Taya.
2Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri
3A manyan ruwaye
4Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku,
5Sa’ad da magana ta kai Masar,
6Ku haye zuwa Tarshish;
7Wannan ce birnin murnanku,
8Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya
9Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi,
10Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu,
11Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku
12Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba,
13Dubi ƙasar Babiloniyawa,23.13 Ko kuwa Kaldiyawa
14Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish;
15A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
16“Ɗauki garaya, ki ratsa birni,
17A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
18Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.