1Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi.
2Ya kai gari cike da hayaniya,
3Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya;
4Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum;
5Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar
6Elam ya ɗauki kwari da baka,
7Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi,
8An rurrushe kāriyar Yahuda,
9kuka ga cewa Birnin Dawuda
10Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima
11Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu
12Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki
13Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna,
14Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa,
16Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini
17“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi
18Zai dunƙule ka kamar ƙwallo
19Zan tumɓuke ka daga makaminka,
20“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin22.23 Ko kuwa kursiyi daraja domin gidan mahaifinsa.
24Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga ’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.