We Believe JesusFé, Esperança e Nova Vida

Zakariya 5

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ · hauçá

← Zakariya 4 Zakariya Zakariya 6 →

1Na sāke dubawa sai ga naɗaɗɗen littafi mai firiya a gabana!

2Sai ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?”

3Sai ya ce mini, “Wannan ce la’anar da za tă ratsa dukan ƙasar; gama bisa ga abin da ya ce a gefe ɗaya, za a kawar da kowane ɓarawo, kuma bisa ga abin da ya ce a ɗaya gefen za a kawar da duk mai rantsuwar ƙarya.

4Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Zan aika shi, zai shiga gidan ɓarawo, da gidan mai rantsuwar ƙarya da sunana. Zai kasance a gidansa yă hallaka gidan da katakon da duwatsun.’ ”

5Sai mala’ikan da yake mini magana ya zo gaba ya ce mini, “Duba ka gani ko mene ne wannan da yake fitowa.”

6Na tambaya na ce, “Mene ne?”

7Sa’an nan aka ɗaga murfin dalman, a ciki kuwa ga mace zaune!

8Ya ce, “Wannan mugunta ce,” ya kuma tura ta cikin kwandon ya rufe da murfin dalman, ya kuma danna da dutse.

9Na ɗaga idona sama, sai ga mata biyu a gabana, iska tana hura fikafikansu! Suna da fikafikai kamar na shamuwa, suka kuma ɗaga kwandon sama.

10Na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Ina za ku kai kwandon?”

11Ya amsa ya ce, “Zuwa ƙasar Babiloniya5.11 Da Ibraniyanci Shinar. Shinar tsohon sunan Babilon ne. Bisa ga Far 11, a wurin ne mutanen dā suka gina gini mai tsayi na saɓo ga Allah, wanda Ubangiji ya sauka ya dagula harsunansu. don a gina masa haikali. Sa’ad da aka gama ginin, za a ajiye shi a ciki.”

← Zakariya 4 Zakariya Zakariya 6 →