1Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah;
2Da hannunka ka kori al’ummai
3Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar,
4Kai ne Sarkina da kuma Allahna,
5Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya;
6Ba na dogara ga bakana,
7amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu,
8A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini,
9Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu;
10Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba,
11Ka ba da mu a cinye kamar tumaki
12Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba
13Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu,
14Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai;
15Dukan yini ina cikin wulaƙanci,
16saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina,
17Dukan wannan ya faru da mu,
18Zukatanmu ba su juya baya;
19Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji
20Da a ce mun manta da sunan Allahnmu
21da Allah bai gane ba,
22Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini;
23Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci?
24Me ya sa ka ɓoye fuskarka
25An kai mu ƙasa zuwa ƙura;
26Ka tashi ka taimake mu;