1Hikima ba ta yin kira ne?
2A ƙwanƙoli a kan hanya,
3kusa da ƙofofin shiga cikin birni,
4“Gare ku, ya mutane, nake kira;
5Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali;
6Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa;
7Bakina yana magana abin da yake gaskiya,
8Dukan kalmomin bakina suna da adalci;
9Ga mai tunani dukansu daidai ne;
10Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa,
11gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja,
12“Ni, hikima, ina zama tare da hankali;
13Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta;
14Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne;
15Ta wurina sarakuna suke mulki
16ta wurina sarakuna suke mulki,
17Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata,
18Tare da ni akwai wadata da girmamawa,
19’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla;
20Ina tafiya a hanyar adalci,
21ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata
22“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa,
23an naɗa ni tun fil azal,
24Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni,
25kafin a kafa duwatsu a wurarensu,
26kafin ya yi duniya ko gonaki
27Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu,
28sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa
29sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa
30A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa.
31ina farin ciki da dukan duniyarsa
32“Yanzu fa, ’ya’yana, ku saurare ni;
33Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima;
34Mai albarka ne wanda ya saurare ni;
35Gama duk wanda ya same ni ya sami rai
36Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa;