1Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can,
3lokacin da fitilarsa take haske a kaina
4Kwanakin da nake tasowa,
5lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni,
6lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa,
7“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna
8matasan da suka gan ni sukan ja gefe
9sarakuna suka yi shiru
10Muryar manya ta yi tsit
11Duk wanda ya ji ni ya yaba mini
12domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako,
13Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka.
14Na yafa adalci ya zama suturata;
15Ni ne idon makafi
16Ni mahaifi ne ga masu bukata;
17Na karya ƙarfin mugaye
18“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana,
19Jijiyoyina za su kai cikin ruwa,
20Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau,
21“Mutane suna mai da hankali su saurare ni,
22Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba.
23Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama.
24Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda;
25Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu;