1Elihu ya ci gaba,
2“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan,
3Daga nesa na sami sanina;
4Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne;
5“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane;
6Ba ya barin mugaye da rai
7Ba ya fasa duban masu adalci;
8Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi,
9yana gaya musu abin da suka yi,
10Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su
11In sun yi biyayya suka bauta masa,
12Amma in ba su saurara ba,
13“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi;
14Suna mutuwa tun suna matasa,
15Amma yana kuɓutar da masu wahala;
16“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci,
17Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye;
18Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki;
19Dukiyarka
20Kada ka yi marmari dare yă yi,
21Ka kula kada ka juya ga mugunta,
22“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa.
23Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi,
24Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa,
25Dukan ’yan adam sun gani;
26Allah mai girma ne,
27“Yana sa ruwa yă zama tururi
28Gizagizai suna zubo da raɓarsu
29Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai
30Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi,
31Haka yake mulkin al’ummai
32Yana cika hannuwansa da walƙiya
33Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa;