1Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2“Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
3Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,
4Manyan tekuna ne wurin zamanki;
5Sun yi dukan katakanki
6Da oak daga Bashan
7Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki
8Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki;
9Masu hikima na Gebal27.9 Wato, Baibilos suna ciki
10“ ‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut
11Mutanen Arfad da Helek
12“ ‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
13“ ‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
14“ ‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
15“ ‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
16“ ‘Mutanen Aram27.16 Da yawa cikin rubuce-rubucen hannu na Ibraniyanci; waɗansu rubuce-rubucen hannu na Ibraniyanci da na Siriyak Edom sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
17“ ‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa,27.17 Ma’anar Ibraniyanci na wannan kalma babu tabbas. da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
18“ ‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
19Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
20“ ‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
21“ ‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da ’yan raguna, da raguna, da awaki.
22“ ‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
23“ ‘Haran, Kanne da Eden da kuma ’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
24A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
25“ ‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama
26Matuƙan jiragenki sun kai ki
27Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki,
28Ƙasashen bakin teku za su girgiza
29Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi
30Za su tā da muryarsu
31Za su aske kawunansu saboda ke
32Yayinda suke kuka a kanki kuwa,
33Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi,
34Yanzu teku ta farfashe ki
35Dukan mazaunan bakin teku
36’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki;