1Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana;
2Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama
3Zan yi shelar sunan Ubangiji.
4Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne,
5Sun aikata mugunta a gabansa;
6Haka za ku biya Ubangiji,
7Ku tuna da kwanakin dā,
8Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu,
9Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa,
10A cikin hamada ya same shi,
11kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta
12Ubangiji kaɗai ya jagorance shi;
13Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse
14da kindirmo da madara daga shanu da tumaki
15Yeshurun32.15 Yeshurun yana nufin mai adalci, wato, Isra’ila. ya yi ƙiba, ya yi kauri;
16Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu,
17Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba,
18Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku;
19Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su,
20Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su,
21Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba,
22Gama fushina ya kama wuta,
23“Zan tula masifu a kansu
24Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu,
25Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su,
26Na ce zan watsar da su
27Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba,
28Al’ummai ne marasa azanci,
29A ce su masu hikima ne har su gane wannan
30Yaya mutum guda zai kore dubu,
31Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne,
32Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne,
33Ruwan inabinsu dafin macizai ne,
34“Ban jibge wannan a ma’ajiya
35Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa.
36Ubangiji zai shari’anta mutanensa
37Zai ce, “To, ina allolinsu,
38allolin da suka ci kitsen hadayunsu
39“Ku duba yanzu cewa ni ne Shi!
40Na ɗaga hannu sama na kuma furta.
41sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya
42Zan sa kibiyoyina su bugu da jini,
43Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa,32.43 Ko kuwa Ku sa mutanensa su yi farin ciki, ya al’ummai
44Sai Musa ya zo da Yoshuwa32.44 Da Ibraniyanci Hosheya, wani sunan Yoshuwa. ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
45Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
46ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce ’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
47Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
48A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
49“Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
50A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
51Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
52Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”