1“Idanuna sun ga waɗannan duka,
2Abin da kuka sani, ni ma na sani;
3Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki,
4Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi;
5In da za ku yi shiru gaba ɗaya!
6Ku ji gardamata yanzu;
7Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah?
8Ko za ku nuna masa sonkai?
9In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi?
10Ba shakka zai kwaɓe ku
11Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro?
12Duk surutanku kamar toka suke;
13“Ku yi shiru zan yi magana;
14Don me na sa kaina cikin hatsari
15Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance;
16lalle wannan zai kawo mini kuɓuta
17Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa;
18Yanzu da na shirya ƙarata,
19Ko wani zai ce ga laifin da na yi?
20“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah,
21Ka janye hannunka nesa da ni,
22Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa,
23Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne?
24Don me ka ɓoye mini fuskarka;
25Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa?
26Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni;
27Ka daure ƙafafuna da sarƙa;
28“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu,